Shugaban Gambia Adama Barrow ya rantsar da kansa a makwabciyar kasar Senegal, yayin da Yahya Jammeh wanda ya dade yana mulkin kasar ya ki sauka daga karagar mulki, lamarin da ya kara dagula rikicin siyasa.
A ranar Alhamis ne aka rantsar da Barrow, wanda ya lashe zaben da aka yi takaddama a kai a ranar 1 ga watan Disamba a wani biki cikin gaggawa da aka shirya a ofishin jakadancin Gambia da ke Dakar babban birnin kasar Senegal.
"Wannan rana ce da wani dan Gambia ba zai taba mantawa da shi ba a rayuwarsa," in ji Barrow a wani jawabi da ya yi kai tsaye bayan an rantsar da shi.
A birnin Dakar, karamin dakin ofishin jakadanci na dauke da mutane kusan 40 da suka hada da firaministan Senegal da kuma shugaban hukumar zaben Gambia.
Haka kuma a wajen taron akwai jami’an kungiyar ECOWAS, kungiyar kasashen yammacin Afirka, wadda ke barazanar shiga tsakani na soji domin tilastawa Jammeh barin mulki.
A jawabinsa na rantsar da shi, Barrow ya kira ECOWAS, da Tarayyar Afirka da Majalisar Dinkin Duniya da su goyi bayan gwamnati da al'ummar Gambia wajen aiwatar da nufinsu.
A farkon makon nan ne Jammeh, wanda ya hau kan karagar mulki a shekara ta 1994, ya kafa dokar ta baci, yayin da majalisar dokokin kasar ta tsawaita wa'adin mulki da kwanaki 90.